エピソード

  • Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
    2025/05/27

    Send us a text

    Najeriya tana cikin ƙasashen da suka fi yawan yara a duniya, a cewar Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF).


    Sai dai a cewar Hukumar ta UNICEF, kusan rabin wadannan yara suna fuskantar kalubale, kama daga cin zarafi zuwa rashin samun kulawa da dai sauran su.
    Wadannan matsaloli da yara suke fuskanta dai sun dade suna ci wa masu ruwa da tsaki tuwo a kwarya.


    Yayin da ake bikin Ranar Yara, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kan halin da ya yara suke ciki a yau.

    続きを読む 一部表示
    25 分
  • Tasirin Dangantaka Tsakanin Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka
    2025/05/26

    Send us a text

    A tsarin mulkin dimokuraɗiyya, dangantaka tsakanin bangaren zartarwa da majalisun dokoki tana taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da shugabanci a tsakanin al’umma.


    A galibin kasashe masu bin tsarin na dimokuraɗiyya, ’yan majalisa kan kasance masu wakiltar al’umma da kare muradunta, da sa ido da kuma bayar da shawarwarin da suka dace ga bangaren zartarwa domin ci gaban kasa.
    Sai dai a Najeriya, a wasu lokutan akan zargi ’yan majalisa da zama ’yan amshin Shata.
    Ko me ya sa haka? Shin yaya ya kamata dangantaka ta kasance a tsakanin banaren zartarwa da majalisar dokoki a tsarin mulkin dimokuraɗiyya?


    Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba.

    続きを読む 一部表示
    24 分
  • Dalilin ’Yan Adawar Najeriya Na Kulla Kawance A Karkashin Inuwar ADC
    2025/05/23

    Send us a text

    Mene ne ya sa jiga-jigan ’yan siyasar Najeriya bangaren adawa suka zabi inuwar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) don hada hannu da nufin kawar da Shugaban Kasa Bola Tinubu da APC dagga mulki?


    Da daren Talata ne dai jigogin adawar, wadanda suka hada da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir Ahmed El-Rufai da kuma dan takarar Shugaban Kasa na Labour Party a 2023, Peter Obi, suka yanke shawarar tsugunawa a karkashin inuwar ADC din.
    Shin ko wannan jam’iyya tana da inuwa mai ni’imar da za ta iya rike wannan hadaka? Shin wadannan ’yan siyasa za su iya ci gaba da shan hannu da juna har su kawar da gwamnati mai ci?


    Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai nazari ne kan karfin da wannan kawance yake da shi na kalubalantar gwamnati mai ci.

    続きを読む 一部表示
    24 分
  • Illar Sare Itatuwa Ga Canjin Yanayi Da Lafiyar Mu
    2025/05/22

    Send us a text

    Shekaru da dama kenan da hukumomin duniya ke gudanar da tarurruka da dama kan zakulo hanyoyin da za a kawo karshen dumamar yanayi a duniya.
    Dumama ko canjin yanayi na cigaba da barazana ga duniya, inda ake samun sauye sauye ga yanayi da wasu abubuwa da masana ke bayyana ka iya kara ta’azzara in ba’ayi wani abu a kai ba.


    Daya daga cikin abubuwan da masana suka bayyana dake kawo wannan matsala itace yadda alumma ke kada itatuwan da aka dasa ba tare da lura da illar da hakan ke jawowa ga muhalli ba.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi Nazari ne kan illar sare itatuwa ba tare da dasa wasu ba kan sauyin yanayi da kuma lafiyar mu.

    続きを読む 一部表示
    30 分
  • Yadda 'Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su
    2025/05/20

    Send us a text

    Kula da lafiya na nufin yin abubuwa da ke kare mutum daga kamuwa da cututtuka da kuma tabbatar da cewa jiki na aiki yadda ya kamata.

    Wannan ya haɗa da cin abinci mai gina jiki, motsa jiki akai-akai, da dai sauran su.
    Sai dai a wannan zamani ‘yan Najeriya ba kasafai suke kula da lafiyar jikin su ba, a mafi yawan lokuta ma sai ciwo ya kwantar da mutum sannan yake tunawa da likita.
    Ko wadanne matakai ya kamata 'yan Najeriya su ringa dauka wajen kare kan su da ma lafiyar jikin su?


    Shirin Najeriya A YAU na wannan lokaci zai yi nazari ne kan yadda 'yan Najeriya zasu dinga kula da lafiyar jikin su.

    続きを読む 一部表示
    25 分
  • Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?
    2025/05/19

    Send us a text

    Daya daga cikin ginshikan tsarin dimokuradiyya shi ne zabi – bai wa jama’a dama su zabi abin da suke so, ko kuma wanda suke so ya shugabance su.


    Wannan ne ya sa daya daga cikin muhimman matakai a kafuwar tsarin shi ne zabe.
    Sai dai kuma abin tambaya shi ne, zabin ya hada har da na yin zabe ko kaurace masa?
    Mene ne matsayin tsarin dimokuardiyya idan aka wajabta wa al’umma kada kuri’a?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba.

    続きを読む 一部表示
    24 分
  • Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
    2025/05/16

    Send us a text

    Jam’iyyar NNPP wadda Dr. Boniface Aniebonam ya kafa a shekarar 2001, ta samu karfi sosai a Jihar Kano bayan tsohon gwamna Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga cikinta a shekarar 2022 tare da mabiyansa na Kwankwasiyya.


    Shigowarsa ta farfado da jam’iyyar, inda ta samu gagarumar nasara a zaɓen 2023 ta hanyar lashe kujerar gwamna da wasu kujerun majalisa.
    Sai dai rikicin cikin gida da rikice-rikicen shugabanci suna ma jamiyyar rauni wanda hakan ya haddasa ficewar wasu manyan ‘ya’yanta zuwa APC, lamarin da ke haifar da tambaya kan makomar NNPP a Kano.
    Shin jam’iyyar NNPP za ta kai labari a Kano, musamman bayan ficewar wasu daga cikin jiga-jiganta?


    Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba.

    続きを読む 一部表示
    24 分
  • Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Dalibai A Jarabawa
    2025/05/15

    Send us a text

    Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta yi amai ta lashe.
    Bayan ta musanta dukkan zarge-zargen da aka yi cewa tana da hannu a rashin kyawun sakamakon jarrabawar da ta shirya, Shugabanta ya fito ya amsa laifi.


    Yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai, Farfesa Is-haq Oloyede ya ce dalibai 379,997 abin ya shafa, kuma hukumar zata sake shirya musu wata jarabawar.


    Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi duba ne a kan dalilan Hukumar ta JAMB.

    続きを読む 一部表示
    20 分