『Najeriya a Yau』のカバーアート

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau

著者: Muslim Muhammad Yusuf Ummu Salmah Ibrahim
無料で聴く

このコンテンツについて

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

© 2025 Najeriya a Yau
政治・政府 政治学
エピソード
  • Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
    2025/05/27

    Send us a text

    Najeriya tana cikin ƙasashen da suka fi yawan yara a duniya, a cewar Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF).


    Sai dai a cewar Hukumar ta UNICEF, kusan rabin wadannan yara suna fuskantar kalubale, kama daga cin zarafi zuwa rashin samun kulawa da dai sauran su.
    Wadannan matsaloli da yara suke fuskanta dai sun dade suna ci wa masu ruwa da tsaki tuwo a kwarya.


    Yayin da ake bikin Ranar Yara, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kan halin da ya yara suke ciki a yau.

    続きを読む 一部表示
    25 分
  • Tasirin Dangantaka Tsakanin Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka
    2025/05/26

    Send us a text

    A tsarin mulkin dimokuraɗiyya, dangantaka tsakanin bangaren zartarwa da majalisun dokoki tana taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da shugabanci a tsakanin al’umma.


    A galibin kasashe masu bin tsarin na dimokuraɗiyya, ’yan majalisa kan kasance masu wakiltar al’umma da kare muradunta, da sa ido da kuma bayar da shawarwarin da suka dace ga bangaren zartarwa domin ci gaban kasa.
    Sai dai a Najeriya, a wasu lokutan akan zargi ’yan majalisa da zama ’yan amshin Shata.
    Ko me ya sa haka? Shin yaya ya kamata dangantaka ta kasance a tsakanin banaren zartarwa da majalisar dokoki a tsarin mulkin dimokuraɗiyya?


    Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba.

    続きを読む 一部表示
    24 分
  • Dalilin ’Yan Adawar Najeriya Na Kulla Kawance A Karkashin Inuwar ADC
    2025/05/23

    Send us a text

    Mene ne ya sa jiga-jigan ’yan siyasar Najeriya bangaren adawa suka zabi inuwar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) don hada hannu da nufin kawar da Shugaban Kasa Bola Tinubu da APC dagga mulki?


    Da daren Talata ne dai jigogin adawar, wadanda suka hada da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir Ahmed El-Rufai da kuma dan takarar Shugaban Kasa na Labour Party a 2023, Peter Obi, suka yanke shawarar tsugunawa a karkashin inuwar ADC din.
    Shin ko wannan jam’iyya tana da inuwa mai ni’imar da za ta iya rike wannan hadaka? Shin wadannan ’yan siyasa za su iya ci gaba da shan hannu da juna har su kawar da gwamnati mai ci?


    Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai nazari ne kan karfin da wannan kawance yake da shi na kalubalantar gwamnati mai ci.

    続きを読む 一部表示
    24 分

Najeriya a Yauに寄せられたリスナーの声

カスタマーレビュー:以下のタブを選択することで、他のサイトのレビューをご覧になれます。